Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Sunday, 6 November 2016

Hare-haren IS sun halaka mutane 21 a Iraki

Kungiyar IS ta ce ita ce ta kai wasu hare-haren
kunar bakin wake biyu a biranen Tikrit da
Samarra na Iraki, inda ta kashe akalla mutane
21.
An kai dukkan hare-haren ne ta yin amfani da
motocin daukar marasa lafiya da aka shake su
da bama-bamai.
An tayar da daya daga cikin bama-baman ne a
kan layin motocin dake jira a bincike su a wurin
duba ababen hawa a Tikrit.
Shi kuma harin na Samarra, an kai shi ne a wurin
da ake ajiye motoci da masu ibada 'yan shi'a ke
amfani da shi.
Jami'ai sun ce 10 daga cikin wadanda suka
mutun 'yan kasar Iran ne.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();