Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Wednesday, 9 November 2016

Kwarewar Lukaku ya wuce zama a Everton — Koeman

Kociyan Everton, Ronald Koeman, ya ce
kwarewar da Romelu Lukaku yake da ita a fagen
murza-leda ya fi karfin ya ci gaba da zama a
kungiyar.
Koeman ya ce "Ina jin Lukaku ya hada komai a
wasan kwallon kafa, ya kware wajen murza leda
ya kuma iya cin kwallo yana da tsawo yana kuma
da karfi".
Kwantiragin Lukaku da Everton za ta kare a
karshen kakar 2019, ya kuma koma kungiyar da
taka-leda ne daga Chelsea, inda yanzu haka ya ci
mata kwallaye 68 a wasanni 137.
Koeman ya kwatanta salon kwallon da Lukaku ke
buga wa da irin wadda tsohon dan kwallon
tawagar Netherlands, Patrick Kluivert ya yi.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();