Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Thursday, 3 November 2016

Mun ji kunya da aka doke mu a gida - Pochettino

Kocin Tottenham Mauricio Pochettino ya ce ba
wasan da suka yi a Wembley ba ne ya sa suka
sha kashi a hannun Bayer Leverkusen a gasar
cin kofin zakarun turai.
Bayer Leverkusen ta doke Tottenham da ci 1-0
ranar Laraba kuma hakan na nufin sun sha kashi
a dukkan wasannin cin kofin turai a gida a bana.
Pochettino ya ce: "Babu inda ba a samun
matsala a kwallon kafa a duk duniya. Matsalar a
wurinmu take ba a Wembley ba."
Tottenham na da zabi ta buga dukkan wasannin
lig na gida da kuma na cin kofin turai a Wembley
a kakar wasa mai zuwa.
Pochettino ya kara da cewa: "Wannan lamari
babban abin kunya ne a gare ni. Ba mu da wani
katabus ganin cewa mun yi wasa biyu a
Wembley, inda Monaco da Bayer Leverkusen,
suka kayar da mu. Laifin a wurinmu yake."

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();