Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Monday, 7 November 2016

Ronaldo zai sa hannu kan ci gaba da wasa a Real Madrid a ranar Litinin

Cristiano Ronaldo ya amince zai saka hannu kan
yarjejeniyar ci gaba da murza-leda a Real
Madrid har zuwa kakar wasan 2021 a ranar
Litinin.
Tun farko kwantiragin Ronaldo mai shekara 31,
da Madrid za ta kare a watan Yunin 2018, idan
ya tsawaita zamansa a kungiyar, za ta cika a
lokacin da ya kai shekara 36.
Ana kuma rade-radin cewar dan wasan tawagar
Portugal zai karbi albashin da zai kai fam
365,000 a kowanne mako.
Ronaldo ya ci kwallaye 371 tun lokacin da ya
koma Madrid da taka-leda daga Manchester
United a shekarar 2009.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();