Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Wednesday, 2 November 2016

FA ta hukunta Jose Mourinho

Hukumar kwallon kafa ta Ingila ta hukunta
kociyan Manchester United, Jose Mourinho, inda
ta ce ba zai ja ragamar kungiyar ba a wasa
daya.
Hukumar ta yanke wannan hukuncin ne, bayan
da alkalin wasa Mark Clattenburg ya bai wa
kociyan jan kati a karawar da United ta tashi
wasa babu ci da Burnley a gasar Premier.
Hukumar ta kuma ci kociyan tarar kudi fam
8,000, haka kuma wasan da United za ta yi da
Swansea ne hukuncin zai yi aiki a kansa.
Haka kuma hukumar ta ci tarar Mourinho kudi
fam 50,000 kan batun da ya yi a kan nada alkalin
wasa Anthony Taylor.
Mourinho ya ce nada Taylor a matsayin wanda
ya hura karawar da suka yi da Liverpool a Anfield
an sa shi cikin matsi.
A bisa doka ba a yadda mai horar da kwallon
kafa ya yi jawabi kan alkalin tamaula kafin a
buga wasa ba.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();