Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Tuesday, 27 December 2016

'Za mu mayar da dajin Sambisa wurin atisayenmu'

Hukumomin soji a Nigeria sun ce za su mayar da dajin Sambisa - inda ya kasance sansanin mayakan Boko Haram tun shekara ta 2013 - wurin atisaye.
A makon jiya ne dai shugaban kasar, Muhammadu Buhari, ya tabbatar da cewa sojojin sun yi nasarar kwace dajin daga hannun mayakan.
Mai magana da yawun rundunar sojin kasa Birgediya-Janar Sani Usman Kukasheka ya shaida wa BBC cewa za a yi hakan ne domin tabbatar da cewa ''wasu miyagun mutane ba su fake a wannan dajin ba.''
Janar Kukasheka ya ce kuma nan gaba kadan za su yi wa 'yan kasar bayanin abubuwan suka tarar a dajin bayan fattatakar mayakan Boko Haram daga sansanoninsu.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();