Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Thursday 12 January 2017

Ba abin da zai hana ni zama shugaban Gambia - Barrow

Wanda ya lashe zaben shugaban kasar Gambia
Adama Barrow ya ce ko ana ha-maza ha-mata
sai ya sha rantsuwar kama aiki a zaman
shugaban kasar Gambia a makon gobe.
A cikin wata hira da BBC Mr. Barrow ya yi kira
ga shugaba mai ci yanzu Yahaya Jammeh da ya
zo su tattauna ido-da-ido domin warware rikicin
siyasar kasarsu gabanin wannan ranar 19 ga
wata Janairu.
Kalaman nasa na zuwa ne sa'o'i gabanin isar
tawagar masu shiga tsakanin ta kungiyar Ecowas
zuwa kasar domin ciwo kan Yahaya Jameh ya
sauka a cikin Lumana.
''Wa'adin mulkinsa zai kare da karfe 12 na dare
na ranar 18 ga wata, don haka a hukumance zan
kasance shugaban kasar ranar 19 ga wata; kuma
ko ana ha-maza ha-mata sai an rantsar da ni'' inji
Barrow.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();