Wellcome to Arewabuzz No:1 networking arena

Like us on Facebook

Friday, 2 December 2016

Wa zai yi nasara tsakanin Man City da Chelsea?

Manchester City za ta karbi bakuncin Chelsea a
gasar cin kofin Premier wasan mako na 14 a
ranar Asabar.
Wannan shi ne karo na 154 da kungiyoyin biyu za
su kece raini a tarihi, inda City ta ci wasanni 52,
Chelsea ta samu nasara a wasanni 62 suka yi
canjaras sau 39.
A gasar cin kofin Premier ta bara, City ce da
doke Chelsea 3-0 a Ettihad, sannan ta kara doke
ta 3-0 a Stamford Bridge, yayin da Chelsea ta
samu nasara a kan City da ci 5-1 a gasar FA.
Chelsea ce ke mataki na daya a kan teburin
gasar Premier da maki 31, yayin da Manchester
City ke matsayi na uku da maki 30.

No comments:

Post a Comment

'; (function() { var dsq = document.createElement('script'); dsq.type = 'text/javascript'; dsq.async = true; dsq.src = '//' + disqus_shortname + '.disqus.com/embed.js'; (document.getElementsByTagName('head')[0] || document.getElementsByTagName('body')[0]).appendChild(dsq); })();